Tsohon Sanatan Kogi Dino Malaye ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin jam’iyyar da ta kawo yunwa da talauci da bala’i a Nigeria
A wani faifan bidiyo da Manuniya ta kalla an ga Sanatan yana cewa “Nigeria zata gyaru sai dai kuma ayi hattara da wannan jam’iyyar APC wacce ta kawo yunwa da talauci da bala’oin da Nigeria ke fama dasu”
Sannan sanatan yayi Allah ya isa tare da cewa “Allah ya isa ba zamu yafe ba ko kabarin ku yana ci da wuta”
Sai dai masana na ganin cewa ai shima sanatan yana cikin wadanda suka kawo jam’iyyar APC ko dayake dai ya barta. Sannan masana na ganin Sanatan Buhari ya tsine mawa tunda dai Gwamnatinsa ke mulki
Kun yarda da kalaman Sanatan?