Contact Information

Theodore Lowe, Ap #867-859
Sit Rd, Azusa New York

We Are Available 24/ 7. Call Now.

Gwamnatin Jihar Kaduna tace KADPOLY da Open University kadai ne za a bude

Za a cigaba da rufe duka sauran makarantu har da A.B,U Zaria saboda COVID-19

Ana sa ran a bude makarantu a Najeriya a ranar Litinin, 18 ga watan Junairu, 2021, bayan tsawon lokacin da aka dauka a gida saboda annobar COVID-19.

Amma a jihar Kaduna, gwamnatin Nasir El-Rufai ta ce za a cigaba da rufe duk wasu makarantun da ke jihar, har da manyan makarantun gwamnatin tarayya.

Jaridar Daily Trust tace Sakatariyar din-din-din ta ma’aikatar ilmi na jihar Kaduna, Phoebe Sukai Yayi, ta bada wannan sanarwa a ranar Lahadi, 17 ga watan Junairu.

Phoebe Sukai Yayi ta bayyana cewa suna lura da yadda cutar COVID-19 ta ke cigaba da yaduwa a Kaduna.

Share:

administrator

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *