Wani daga cikin manyan APC a kudancin Najeriya, Ayogu Eze, ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba, jam’iyyarsu za ta samu karin wasu gwamnoni.
Jaridar The Sun ta rahoto Mista Ayogu Eze ya na cewa akwai gwamnonin jam’iyyar PDP da za su fice su sauya-sheka, su dawo cikin tafiyar APC mai mulki.
Eze wanda ya tsaya a matsayin ‘dan takarar gwamnan jihar Enugu a jam’iyyar APC ya yi wannan jawabi ne lokacin da ya raba kayan bikin sabuwar shekara.
Da ya ke rabawa ‘ya ‘yan jam’iyyar ta su ta APC wadannan kaya, an rahoto Eze ya na cewa:
Eze ya ce yanzu APC ta na kara shiri, ta na hada-kai da sauran jam’iyyu domin ta yi nasara a 2023.
“Ina so kuma in fadu maku a madadin shugabanninmu ba mu sakakance ba, APC tana zama wata amarya a Kudu maso gabas, jihar Ebonyi ta fadi, Imo ta fadi.”