Wasu jiga-jigan jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) su shida a karamar hukumar Oyibo da ke jihar Ribas, sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Hakan na zuwa ne duk da rikicin da ya rincabe a jam’iyyar, sakamakon dakatar da wasu yayanta da aka yi, jaridar The Nation ta ruwaito.
Masu sauya shekar, Adolphus Nweke, Onyema Ihenna, Ibekwe Okere, da sauransu, sun ce PDP ba jam’iyya mai inganci bace.
Suna burin cewa tsarin jam’iyyar zai kara karfi bayan wannan lokaci da ake ciki na rikice-rikice.